Rahotanni sun ce wasu ƴan bindiga sun tayar da bam a titin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna da ke ɗauke da fasinja 970.
Rahotanni sun ce maharan sun yi nasarar hana jirgin tafiya, inda suka buɗe wuta.
Ɗaya daga cikin fasinjan da ke cikin jirgin ya tabbatar wa BBC da harin, inda ya ce maharan sun kwashi mutane sun tafi da su. Sannan jami'an tsaron da ke cikin jirgin sun yi musayar wuta da ƴan bindigar.
Ya ce sun kashe mutum guda.
Wani ma'aikacin tashar jirgin a Rigasa ya shaida wa BBC cewa "jirgin ya kamata ya iso misalin ƙarfe 8:20 amma har yanzu ba labari."
Hukumomin sufurin jiragen ƙasa ta Najeriya da hukumomin gwamnatin Kaduna ba su tabbatar da al'amarin ba.
Read full article
- Major Ugandan highway declared safe after bomb scare
- GAF commits 1,250 troops to combat terrorism
- 'Installation' of new Bawku Naba could escalate existing conflict - Security Analyst warns
- Bawku conflict: 5,000 additional soldiers to be deployed by close of week
- Blame politicians for the Bawku conflict - Vladimir Antwi-Danso
- Read all related articles