BBC

News

Entertainment

Sports

Business

Africa

Live Radio

Country

Webbers

Lifestyle

SIL

An tuhumi Diezani Alison-Madueke kan zargin cin hanci a kotun Birtaniya

D2401200 40fa 11ee 9b58 Cb80889117a8 Diezani Alison-Madueke

Tue, 22 Aug 2023 Source: BBC

Hukumar yaƙi da manyan laifuka a Birtaniya ta tuhumi tsohuwar ministar man fetur ta Najeriya a kotu, kan laifukan cin hanci.

Ana zargin Diezani Alison-Madueke da karɓar cin hancin miliyoyi barkatai na fam ɗin Ingila daga kwangilolin man fetur da iskar gas, da ta bayar don samun cin hanci.

Wata sanarwa da sashen yaƙi da cin hanci da rashawa na duniya a Hukumar Yaƙi da Manyan Laifuka ta Ƙasa ta ce ana zargin Diezani ta ci gajiyar aƙalla fam 100,000 kuɗi hannu, da samun zungura-zunguran motocin alfarma da tafiye-tafiyen jirgin sama na shata, da tafiya hutun alfama da kuma kadarori birjik a London.

Shugaban sashen yaƙi da cin hanci na ƙasashen duniya, Andy Kelly ya ce, "waɗannan tuhume-tuhume, muhimmin abu ne na wani cikakken bincike da sarƙaƙiya a cikin ƙasashen duniya."

Diezani Alison-Madueke, 'yar shekara 63, ta kasance a matsayin Shugabar Ƙungiyar ƙasashe Masu Arziƙin Man Fetur (OPEC), kuma ministar man fetur ta Najeriya a tsakanin 2010 zuwa 2015.



Read full article

Source: BBC