Mon, 19 Jul 2021
Source: BBC
Dan kwallon Manchester City, mai buga wa tawagar Jamus tamaula 'yan kasa da shekara 21, Lukas Nmecha ya koma Wolfsburg.
Mai shekara 22 ya taka rawar gani a wasannin aro da ya yi a Anderlecht ta Belgium a kakar da ta kare, wanda ya ci kwallo 21 a wasa 41 da ya yi.
Nmecha, wanda aka haifa a Humburg ya wakilci tawagar kwallon kafar Ingila ta matasa a mataki da yawa, ya kuma buga wa Wolfburg wasa a 2019-20.
Ya buga wa City karawar Carabao Cup da wasa biyu a Premier League.
Read full article
Source: BBC