Rundunar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ayyana daukar matakai bakwai da ta ce za su kawo sauki game da hare-haren da 'yan bindiga suke kai wa al'ummar jihar.
Eata sanarwa da Kwamishinan rundunar, Ayuba N. Elkanah ya aike wa manema labarai ranar Lahadi ta jaddada matakin da gwamnan jihar Mohammed Bello Matawalle ya bayar da umarnin dauka domin shawo kan matsalar.
Mun zayyano matakan kamar yada Kwamishina ya bayyana:
Mahukunta sun yi amanar cewa gungun 'yan bindigar suna amfani da wadannan ayyukan tattalin arziki don kai hare -haren ga al'ummomi.
Kwamishinan 'yan sandan jihar Zamfara, Ayuba Elkanah, ya shaida wa manema labarai a Gusau babban birnin kasar, cewa an umarci hukumomin tsaro da su aiwatar da sabbin matakan da gwamnati ta sanar.
Najeriya na fama da matsalar kashe-kashen mutane da ta yi muni da kuma yan bindigar da ke sace mutane don karbar kudin fansa .
Ga dukan alamu hukumomi da iyalai da kuma al'umomi suna ɗaukar matakai don shawo kan matsalar.
Read full article