Mai tsaron bayan Manchester City, Ruben Dias ya tsawaita yarjejeniyar ci gaba da taka leda a Etihad zuwa karshen 2027.
Dan kwallon tawagar Portugal, mai shekara 24 ya koma City da taka leda kan kwantiragin kaka shida a Satumbar 2020 kan fam miliyan 65.
Ya bayar da gudunmuwar da City ta ci Premier League da Carabao Cup da kai wa wasan karshe a Champions League a bara.
Dias shine ya lashe kyautar dan wasan da ba kamarsa da kungiyar marubuta labarin wasanni da ' kungiyar 'yan kwallon Premier League ta karrama a kakar da ta wuce.
Dan kasar Portugal ya buga wa City karawa 50, kuma shine ya lashe kyautar mai tsaron baya da ba kamarsa a Champions League a 2020-21.
Ranar Asabar 28 ga watan Agusta, City ta doke Arsenal 5-0 a wasan mako na uku a gasar Premier League a Etihad.
Read full article